Da Gaske ’Yan Arewa Ba Sa Fita Kasashen Waje?
Daga Laraba
More Info
Daga Laraba
Da Gaske ’Yan Arewa Ba Sa Fita Kasashen Waje?
Oct 02, 2024
Muslim Muhammad Yusuf, Ummu Salmah Ibrahim

Wata muhawara da ta karade shafukan sada zumunta a kwanakin nan ita ce ko ’yan Arewa, musamman Hausawa, suna fita kasashen waje.

Duk da wannan ba wani sabon abu ba ne, batun ya dauki sabon salo ne a shafukan sada zumunta, musamman Facebook da TikTok, inda ’yan kudancin Najeriya suke wallafa fayafayen bidiyo suna tambayar: shin Hausawa suna zuwa kasashen waje?

Shirin Daga Laraba na wannan makon zai yi duba ne kan wannan batu.