Hukumar Lafiya ta Duniya ta lissafa zazzaɓin Dengue cikin cutuka masu barazana ga bil'adama a fadin duniya.
A 'yan kwanakin Cibiyar yaƙi da cutuka masu yaɗuwa ta Najeriya (NCDC) ta ce ana zargin sama da mutum 71 sun kamu da cutar zazzaɓin Dengue, yayin da tuni aka tabbatar cewa mutum 13 sun harbu da ita a jihar Sokoto.
Shirin Najeriya a Yau ya maida hankali kan matakan da ya kamata ku dauka na kariya da wasu abubuwan da ya kamata ku sani kan cutar Dengue.