Majalisar Dokokin Jihar Kaduna ta soke dokar da ta kirkiri hukumomin raya wasu biranen jihar uku.
Wannan mataki dai ya haifar da zazzafar muhawarar a kan nasabarsa da nuna yatsa da ake yi a tsakanin gwamnati mai ci da wadda ta gada.
Shirin Najeriya a Yau zai binciki dalilin daukar wannan mataki da yadda zai shafi ci gaban kananan hukumomin da abin ya shafa.