Najeriya a Yau
Shiri ne na minti 15 dake duba na tsanaki, da nazari mai gamsarwa, tare da tsokaci mai amfanarwa, a kan batutuwan da ke ɗaukar hankali a lamuran yau da kullum.
Najeriya a Yau
Matsayin Daukar Doka A Hannu A Mahangar Shari’a
•
Halima Djimrao, Muhammad Auwal Sulaiman, Bilkisu Ahmed
Mene ne kundin tsarin mulkin Najeriya ya ce kan wanda aka fusata shi ya dauki doka a hannunsa?
Tun bayan abin da ya faru na zargin batanci ga Annabi Muhammad (SAW) a Sakkwato da daukar matakin da matasan Musulmi suka yi na halaka wacce ta yi batancin nan take, jama’a ke ta musayar ra’ayi kan matsayin shari’a kan wannan batu.
Wakilinmu a Jihar Sakkwato ya fada mana halin da jihar ke ciki, mun kuma ji ta bakin wani mai fashin baki kan dokokin kasa kan abin da ya faru.