Yau ce Ranar Fassara ta Duniya wadda Majalisar Dinkin Duniya ta ware don jinjina ga ayyukan kwararrun da suke hada al'ummomi waje daya, da karfafa zaman lafiya da tsaro a duniya ta hanyar juya bayanai daga wani harshe zuwa wani.
Albarkacin wannan rana, shirin Najeriya A Yau zai tattauna ne kan irin gudunmawar da fassara ke bayarwa wajen habbaka harshen Hausa.