Yayin da halin kuncin da ’yan Najeriya suke fama da shi yake karuwa, yawan masu kira da a dawo da tallafin man fetur ma sai karuwa yake yi.
Sai dai kuma wani hanzari ba gudu ba: shin me zai faru idan da za a dawo da tallafin?
Wanne hali tattalin arzikin Najeriya zai shiga?
Shirin Najeriya A Yau zai yi kokarin amsa wadannan da ma wasu tambayoyin masu alaka da su.