Tanadin Dokar Kasa Kan Kirkirar Gwamnatin Bibiya A Kano
Najeriya a Yau
Najeriya a Yau
Tanadin Dokar Kasa Kan Kirkirar Gwamnatin Bibiya A Kano
Feb 20, 2025
Muslim Muhammad Yusuf, Ummu Salmah Ibrahim

Send us a text

Tun bayan bayyana kafa Gwamnatin Bibiya ko kuma Shadow government a turance da wata kungiya karkashin jamiyyar APC a jihar kano tace zata yi ne  ne dai alumma da dama keta jefa ayar tambaya kan halascin wannan gwamnati.


Kungiyar dai ta bayyana cewa zata kafa wannan gwamnati ne don bibiyan ayyukan gwamnatin gwamna Abba Kabir  Yusuf don tabbatar da ana abin da ya kamata.

Sai dai wannan sanarwa na cigaba da yamutsa hazo inda wasu ke kallon halascin wannan gwamnati.


Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne kan halascin kafa wannan gwamnatin Bibiya a jihar Kano.